Birbishin Rikici

Episode 128

Yadda Uwa Ta Yi Jiran Labarin Garkuwa Da Yayanta

8 mins
6 Jun 20268 minsBirbishin Rikici

Episode description

Lokacin Ramadan ne, kuma Bintu Suleiman, wata uwa kuma ‘yar kasuwa mai shekaru 55 daga Ngoshe a Jihar Borno, Arewa maso Gabashin Najeriya, tana shirin buɗe baki tare da iyalanta.

Sai harbe-harbe ya fara, kuma cikin awa guda gidanta ya kama da wuta. Yayin da ‘yan ta’adda ke tattara mutane, ta samu damar tserewa tare da wasu daga cikin ‘ya’yanta da jikokinta zuwa cikin daji. Daga baya, ta gane cewa mutum huɗu daga cikinsu ba su tsere tare da ita ba. Suna wani wuri a cikin duwatsu.

A wannan shirin na #BIRBISHINRIKICI, mun ga yadda bayan harin, Bintu, wadda yanzu ta rasa matsuguninta, ke samun mafaka a wata makarantar firamare ta gwamnati a Pulka, yayin da har yanzu ba ta san halin da ‘ya’yanta da jikokinta suke ciki ba.

Support Our Journalism

There are millions of ordinary people affected by conflict in Africa whose stories are missing in the mainstream media. HumAngle is determined to tell those challenging and under-reported stories, hoping that the people impacted by these conflicts will find the safety and security they deserve.

To ensure that we continue to provide public service coverage, we have a small favour to ask you. We want you to be part of our journalistic endeavour by contributing a token to us.

Your donation will further promote a robust, free, and independent media.

Donate Here